– Wasu wadanda ake zargin yin fyade an kama su an tafi da su Calabar saboda yaudarar yan mata 2 da suka yi
– Wasu samari guda 2, wadanda aka bayyana suna amfani da suna da hoton mata a Facebook dan su yaudari mutane
– An kama su bayan rohoton da yan sanda suka samu daga wasu da suka yi ma haka
Kamar yadda wani mai amfani da dandalin sadarwa na Facebook Esame Nkim ya bayyana a shafinsa na Facebook cewa samarin suna da bidiyon kansu suna ma yan matan fyade, shi yasa su ka ce ma yan matan su biya kudi N30,000 ku kuma su saka bidiyon a yanar gizo.
Wannan abun ya faru da gaske a gurin aiki na, hoton samarin da kuke gani a kasa. Wadan nan yaran suna amfani da sunan mata da hotunan mata a dandalin sadarwa na facebook.
Sun gayyaci wasu yan mata da suka hadu a facebook dan su zama abokai , yayi da yan matan suka zo adireshin da suka basu no.1 Atekong Calabar. Samarin sai suka ba wasu yan mata wayar su dan su tare su, bayan sun basu abun sha sai suka bace.
Daga sai samari 5 suka shigo suka yan matan 2 fyade, kuma suka dauki bidiyon aika-aikar da su kai masu, daga baya sai suka umurci yan matan akan dole su biya N30,000 ko kuma su saka bidiyon a yanar gizo, sun nuna ma yan mata wani bidiyo da sukayi da wasu yan mata da abin da suka biyasu. Lokacin da sukaje neman kudin, kawai sai suka yanke shawarar kai kara ga hukuma. Sai hukuma ta dauki mataki.
Kusan irin mutanen da zaku yi abota da su.
Leave a Reply